Connect with us

Jigawa

Jigawa: Mutane 2 sun rasu 7 sun jikkata sakamakon rikicin Manoma da Makiyaya

Published

on

A kalla mutane biyu ne suka rasa rayukansu yayin da wasu bakwai suka jikkata sakamakon rikicin da ya barke tsakanin manoma da makiyaya a garin Dagaceri a karamar hukumar Birniwa, ta jihar Jigawa.

 

Rahotonni sun bayyana cewa rikicin ya ɓarke ne bayan wani sabani da aka samu tsakanin wani makiyayi da manomi, wanda daga bisani ya rikide ya zama rikici mai tsanani tsakanin al’ummomin yankin.

 

Jami’an tsaro sun isa wajen da lamarin ya faru domin dawo da doka da oda, yayin da aka tabbatar da cewa an kwashe waɗanda suka jikkata zuwa asibiti domin ba su kulawar jami’an lafiya.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!