Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Addini

Jiragen yaƙin Isra’ila sun ci gaba da luguden wuta kan Zirin Gaza da safiyar laraba

Published

on

Rahotanni daga gabas ta tsakiya na cewa jiragen yaƙin sojin Isra’ila sun ci gaba da luguden wuta a Zirin Gaza da ke yankin Palastinu a wayewar garin yau laraba.

 

Rahotanni sun ce tun a cikin daren jiya sojojin Isra’ila suke ta kai hare-hare ta sama a birnin lamarin da ya yi sanadiyar mutuwar mutane  masu yawa.

 

Wasu mazauna birnin sun bayyana cewa, hare-haren ya shafi muhimman wurare na birnin ciki har da ofisoshin gwamnati.

 

Gidan talabijin na Aljazeera ya ruwaito cewa, a unguwar Tel al-Hawa, wani magidanci da matar sa mai dauke da juna biyu da kuma ɗansu ɗan shekara biyar sun rasa rayukansu sakamakon hari ta sama da jiragen yaki na Isra’ila suka kai a gidansu.

 

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!