Labarai
JNI ta bukaci Tinubu ya gaggauta tsige SHUGABA INEC

Kungiyar Jama’atu Nasril Islam ta Najeriya, ta bukaci Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu da ya gaggauta tsige Shugaban Hukumar Zabe INEC, Farfesa Joash Amupitan.
Sakataren Janar na kungiyar, Farfesa Khalid Abubakar Aliyu, ya bayyana hakan yayin taron shekara-shekara da kungiyar ke shiryawa domin tunkarar watan azumin Ramadana.
Ya ce, kiran ya zama dole sakamakon abin da kungiyar ta zargi shugaban INEC da aikatawa, ciki har da nuna wariya ga Musulunci da Musulmi, da kuma rubuce-rubucen da ya yi da ke ikirarin cewa ana kashe Kiristoci a Najeriya.
Kungiyar ta ce matakin da ta nema yana da muhimmanci domin kare hadin kan kasa da kuma tabbatar da adalci a harkokin zabe a kasar nan.
You must be logged in to post a comment Login