Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Kamfanin NNPC ya bayyana tabbacin cewar yana da ishasshen man fetur

Published

on

Kamafanin main a kasa NNPC ya baiwa masu ababen hawa tabbacin cewa yana da isasshen Man fetur da dangoginsa da za su isa ga jama’a, duk da yunkurin Kungiyar Kwadago ta kasa NLC na tsunduma yaji aikin sai baba ta gani a gobe Talata.

Wannan tabbaci na fitowa ne ta cikin wata sanarwa da mai magana da yawun kamfanin Ndu Ughamadu ya bayar jiya a Abuja.

Sanarwar ta kara da cewa Kamfanin ya na da isasshen Man Fetur da albarkatunsa za a samarwa al’umma na tsawon kwanaki 39, a don haka babu wani abin damuwa dangane da barazanar karancinsa.

Ndu Ughamadu ya shawarci jama’a musamman masu ababen hawa da ka da su firgita ballantana su shiga saye tare da tara Man a gidajensu.

Sannan ya bukaci a gaggauta sanar da su da zarar an samu wani gidan Mai da ke yunkurin boye Man ko kuma aikata wani abu da ya sabawa doka.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!