Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kasuwanci

Kana boye kayan masarufi mu kuma zamu fasa shagon mu rabawa jama’a – Muhyi Magaji

Published

on

Hukumar karbar korafe-korafe da yaki da cin hanci da rashawa ta jihar Kano ta alakanta hauhwar farashin kayayyakin masarufi da cutar corona.

Shugaban hukumar Barista Muhyi Magaji Rimingado ne ya bayyana haka ta cikin shirin Barka da Hantsi na nan Freedom rediyo da safiyar yau.

A cewar Muhyi Magaji tun bayan bullar cutar corona kamfanoni ba sa iya sarrafa kayayyaki kamar yadda ya kamata.

Ya ce, sun tattauna da kamfanoni da dama musamman masu sarrafa sukari, wadanda suka tabbatar da cewa daga farkon azumi zuwa karshensa akwai wadatattceen sukari da zai wadatar da al’ummar Jihar Kano.

Ya kuma jaddada cewa hukumar ba za ta bar ‘yan kasuwa su yi abin da suka ga dama ba a lokacin azumi.

‘‘Domin duk wanda muka kama ya boye kayayyakin masarufi zamu fasa shagon mu rabawa jama’a’’ a cewar Muhyi Magaji Rimingado.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!