Labarai
Kano: Ɗaurarru 52 sun fara rubuta jarabawar NECO da NABAIS

Aƙalla ɗaurarru 52 sun fara rubuta jarabawar NECO da NABAIS a Kano
Aƙalla ɗaurarru 52 da ke gidajen ajiya da gyaran hali a Jihar Kano sun fara rubuta jarabawar kammala sakandare ta NECO da kuma ta Hukumar Kula da Ilimin Larabci da Addinin Musulunci (NABAIS) ta shekarar 2026.
Mai magana da yawun hukumar a jihar Kano, CSC Musbahu Lawan Kofar Nassarawa, ne ya tabbatar da hakan cikin wata sanarwa ta murya da ya aikewa manema labarai.
Ya ce daga cikin ɗaurarrun akwai maza 41 da mata 11, waɗanda aka zabo daga cibiyoyin ajiya da gyaran hali daban-daban na jihar domin rubuta jarabawar.
A cewarsa, wannan shiri na daga cikin ƙoƙarin Hukumar Gidan Gyaran Hali na amfani da ilimi wajen gyara halayen ɗaurarru tare da shirya su domin komawa cikin al’umma bayan kammala wa’adin hukuncinsu.
You must be logged in to post a comment Login