Labarai
NBA ta zargi ƴan Sanda da tsare wani lauya ba bisa ƙa’ida ba

Ƙungiyar Lauyoyi ta Najeriya NBA reshen jihar Kano, ta zargi Rundunar ƴan Sandan Jihar da tsare wani lauya Barista Mustapha Abubakar Adam ba bisa ƙa’ida ba.
NBA, ta bayyana hakan ne ta cikin wata sanarwa da shugaban ƙungiyar Barista Sani Ammani, ya fitar a yau Juma’a.
Sanarwar ta bayyana cewa an tsare lauyan ne a Sashen binciken manyan laifuka na rundunar ƴan sandan Kano a ranar 30 ga Yunin bana, bayan ya nuna rashin jin daɗinsa kan hana shi shiga domin kare wanda ya ke wakilta, yayin da ake barin wasu mutane suna shiga ba tare da tsaiko ba.
Sanarwar ta ci gaba da cewa, daga bisani an sake shi da tsakar dare bayan shugabannin ƙungiyar sun shiga tsakani.
Haka kuma, sanarwar ta kuma ce shugabannin NBA na jihar Kano na NBA Ungogo sun gana da Kwamishinan ƴan Sanda da mataimakinsa mai kula da sashen binciken manyan laifuka domin sasanta lamarin.
Sannan ƙungiyar ta ce, ta samu umarnin kotu da ya hana sake kama lauyan, amma daga bisani an gayyace shi domin gurfana a gaban Kotun Majistare mai lamba 54 da ke Gyadi Gyadi
Kungiyar tayi kira ga mambobinta su halarci zaman kotun domin nuna goyon baya ga lauyan.
You must be logged in to post a comment Login