Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Kotu a Kano ta yanke wa Baturen da ya kade Bahaushe a mota hukunci

Published

on

Babbar kotun jiha mai lamba 11 a nan Kano ta yanke wa wani Bature biyan kudi har Naira miliyan 13 ga matashin da ya kade da Mota lokacin da yake sauri, a wani mumunan hatsari da ya afku a titin rukunin masana’antu na Sharada.

A ranar Talata ne kotun ta kawo karshen shari’ar Baturen mai suna John Bouton dake aiki a wani kamfani dake rukunin masana’antu na Sharada dake Kano.

An tuhumi Baturen ne da laifin yin awon gaba da matashin yayin da yake tafiya a kafa, a cikin shekarar 2015, wanda ya sanya matashin ya shigar da kara a kotun.

Karin labarai:

Yanzu-yanzu: Kotu ta dakatar da Anti-Corruption daga bincikar Sarkin Kano

Kotu ta shawarci masu zuba hannun jari a Kano

Da yake yanke hukunci, mai Shari’a Rabi’u Abubakar Sadiq ya ce Baturen John Bouton zai biya Naira Miliyan 13 kuma za a bayar da Miliyan 5 da dubu dari nan take, sai kuma cikon miliyan 8 da za a rika biya a duk wata ga matashin.

Bayan fitowa daga kotun Freedom Radio ta zanta da lauyan mai kara Abdul Adamu Fagge wanda ya ce yayi farin ciki da wannan nasara da suka samu a shari’ar.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!