Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Zaɓen ƙananan hukumomi ya fi kama da wasan kwaikwayo – PDP tsagin Kwankwaso

Published

on

Jam’iyyar PDP tsagin tsohon Gwamna Kwankwaso ta ce, zaɓen ƙananan hukumomi da aka yi a Kano wasan kwaikwayo ne.

Sakataren yaɗa labaran jam’iyyar Bashir Sanata ne ya bayyana hakan ta cikin wani saƙon bidiyo da ya fitar a shafinsa na Facebook wanda ya karaɗe kafafen sada zumunta.

Sanata ya ce, suna godiya ga ƴan jam’iyyarsu bisa bin umarnin da suka bayar na a ƙauracewa zaɓen.

A cewar sa, rashin fitowar jama’a a zaɓen na nuna cewa al’ummar Kano na tare da su ɗari bisa ɗari.

Karin labarai:

An cafke Budurwa mai garkuwa da mutane a Kano

Kano: Yawan ƙuri’un zaɓen ƙananan hukumomi sun zarce na zaɓen Gwamnan 2019

Sai dai tuni ɓangaren Aminu Wali na jam’iyyar ta PDP suka ce, sun shiga kuma an kara da su a zaɓen, yanzu haka ma sun shiga tattara bayanai domin ɗaukar mataki na gaba.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!