Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Uwar jam’iyyar PDP ta yi magana bayan korar Kwankwaso

Published

on

Uwar jam’iyyar PDP ta ƙasa ta amince da shugabancin jam’iyyar a Kano na tsagin tsohon gwamna Kwankwaso.

Hakan na cikin sanarwar da mai magana da yawun jam’iyyar na ƙasa Kola Ologbondiyan ya fitar.

A cikin sanarwar ya ce, kwamitin ayyuka na jam’iyyar shi ne ya sanya idanu kan zaɓen shugabannin jam’iyyar da aka yi a ranar Asabar wanda tsagin Kwankwaso ya samu kafa shugabanci.

A cewarsa, Shehu Wada Sagagi da sauran shugabanni da aka zaɓa lokaci guda, su ne halastattun shugabannin jam’iyyar a Kano, wanda za su shafe shekara huɗu a kan mulki.

Karin labarai:

Siyasar Kano: Dalilan korar Kwankwaso daga PDP

Siyasar Kano: An ja layi tsakanin Sha’aban da Ganduje

Hakan dai ya biyo bayan zaɓen da tsagin Aminu Wali suka yi a ranar Alhamis inda suka zaɓi sabon shugabanci ƙarƙashin Muhamminna Baƙo Lamiɗo.

Bayan nan kuma suka sanar da korar tsohon gwamna Kwankwaso.

Dama dai tun a Alhamis ɗin tsagin Kwankwaso su ka yi watsi da batun korar ta bakin mai magana da yawun jam’iyyar na Kano Bashir Sanata.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!