Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Muna kan nazarin sakamakon zaɓen ƙananan hukumomi – PDP tsagin Aminu Wali

Published

on

Jam’iyyar PDP ta jihar Kano tsagin Aminu Wali ta ce, tana tattara bayanai domin ɗaukar mataki na gaba kan sakamakon zaɓen ƙananan hukumomi.

Shugaban tsagin Muhammina Baƙo Lamiɗo ne ya bayyana hakan ga Freedom Radio.

Lamiɗo ya ce, dama an saba hakan, duk inda aka yi zaɓen ƙananan hukumomi jam’iyya mai mulki ta lashe baki ɗaya.

Sai dai ya ce, ya zama tilas su shiga a matsayinsu na ƴan adawa da tsammanin ko za a yi musu adalci.

A halin yanzu ya ce, suna tsaka tattara bayanai kan zaɓen domin ɗaukar matakin da ya dace.

Karin labarai:

Har yanzu ba a saki sakamakon jarrabawar NECO na ɗaliban Kano ba

Saura ƙiris na kori Aminu Wali daga PDP – Kwankwaso

Tsagin jam’iyyar na tsohon gwamna Kwankwaso dai sun ƙauracewa zaɓen, ta ha har ƙin shiga takara sannan suka umarci mabiya su ƙauracewa rumfunan zaɓe.

Sai dai Lamiɗo ya ce, su sun shiga kuma an yi zaɓe tare da su.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!