Labarai
Kano: Za a gwada ƙwaƙwalwar matar da ake zargi da hallaka ƴaƴanta
![](https://freedomradionig.com/wp-content/uploads/2020/12/Hauwau-Habib.jpg)
Kotun majistiri mai lamba biyar da ke gidan Murtala ƙarƙashin mai shari’a Hauwa Lawan Minjibir ta fara sauraron shari’ar matar da ake zargi da hallaka ƴaƴanta.
A yayin zaman shari’ar na ranar Talata lauyan gwamnati Barista Lamiɗo Abba Soronɗinki ya karanto mata tuhumar da ake mata.
Ana zargin matar ne da hallaka ƴaƴanta biyu a watan Oktoban da ya gabata, a ƙaramar hukumar Gwale zargin da Hauwa’un ta musanta.
Lauyar wadda ake zargi Barista Huwaila Muhammad Ibrahim ta nemi kotu ta amince a kai wadda ake zargin asibiti domin duba ƙwaƙwalwarta.
Kotun ta amince da buƙatar, inda ta sanya ranar 5 ga watan Janairu na shekara mai zuwa domin ci gaba da shari’ar.
You must be logged in to post a comment Login