Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Kano: Za a gwada ƙwaƙwalwar matar da ake zargi da hallaka ƴaƴanta

Published

on

Kotun majistiri mai lamba biyar da ke gidan Murtala ƙarƙashin mai shari’a Hauwa Lawan Minjibir ta fara sauraron shari’ar matar da ake zargi da hallaka ƴaƴanta.

A yayin zaman shari’ar na ranar Talata lauyan gwamnati Barista Lamiɗo Abba Soronɗinki ya karanto mata tuhumar da ake mata.

Ana zargin matar ne da hallaka ƴaƴanta biyu a watan Oktoban da ya gabata, a ƙaramar hukumar Gwale zargin da Hauwa’un ta musanta.

Lauyar wadda ake zargi Barista Huwaila Muhammad Ibrahim ta nemi kotu ta amince a kai wadda ake zargin asibiti domin duba ƙwaƙwalwarta.

Kotun ta amince da buƙatar, inda ta sanya ranar 5 ga watan Janairu na shekara mai zuwa domin ci gaba da shari’ar.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!