Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Jigawa

An yi garkuwa da malamin makaranta a jihar Jigawa

Published

on

Rundunar ‘yan sanda a jihar Jigawa ta tabbatar da cewa masu garkuwa da mutane sun sace wani malamin makaranta a karamar hukumar Auyo ta jihar.

Malamin mai suna Abdullahi Sani mai shekaru 35, ‘da ne ga wani dan siyasa a jihar, kuma malami ne a makarantar sakandare ta Birniwa a bangaren koyar da darasin Arabiyya.

Rahotanni sun bayyana cewa, masu garkuwa da mutanen sun dira gidan na sa ne da ke unguar Shagari, inda nan take suka yi awon gaba da shi.

Ta cikin sanarwar da jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Jigawa Abdu Jinjiri ya fitar a jiya lahadi, ta bayyana cewa tuni suka fara gudanar da bincike kan lamarin.

Sanarwar ta bayyana cewa, lamarin ya faru ne da karfe biyu na daren jiya a wanda kuma tuni masu garkuwa da shi suka tafi da wayarsa.

 

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!