Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Wakilan Kasashen 70 za su aikin magance kwararar baki

Published

on

Wakilan wasu kasashen duniya 70 sun amince su yi aiki tare don magance matsalar kwararar baki a kasashe da dama, matakin da ke nuna goyan bayan shirin Majalisar Dinkin Duniya wanda wasu kasashe suka janye daga ciki.

Yayin da duniya ke fama da matsalar baki Yan gudun hijira sama da miliyan 21, daukacin kasashe 193 na Majalisar Dinkin Duniya banda Amurka, sun amince da wani daftari a watan Yuli da zai taimaka wajen dakile kwararar baki da kuma kula da su yadda ya kamata.

A taron da zai gudana a yau Litinin da gobe Talata a Morocco, ana saran wakilan kasashen duniya za su amince da daftarin, duk da ya ke wasu kasashen Turai da suka fada karkahsin ikon ‘yan ra’ayin rikau irin su Austria da Hungary da Poland na adawa da shirin.

Wasu Magadan Gari da suka halarci taron da ya gudana a Marakesh a karshen mako, kamar na Saliyo Yvonna Aki-Sawyerr da Marvin Rees na Bristol da ke Birtaniya sun bayyana muhimmanci cimma yarjejeniya domin shawo kan matsalolin da ke haifar da kaurar jama’a.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!