Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Karancin abinci da wutar lankarki ya janyo na sauke ministoci na – Buhari

Published

on

Fadar shugaban ƙasa ta ce, kafin shugaba Buhari ya sauke ministocin sa biyu sai da yayi la’akari da yadda ƙasar ke fuskantar ƙarancin abinci da kuma hasken lantarki.

Mai bai wa shugaban ƙasa shawara na musamman kan harkokin yaɗa labarai Femi Adesina ne ya sanar da hakan yayin zantawar sa da gidan talabijin na Channels.

Ya ce, samar da abinci da gyaran harkokin wutar lantarki muhimman abubuwa ne da shugaba Buhari ya sanya su a gaba, don samarwa da al’umma walwala.

Adesina ya kuma ce, ministocin da aka sauyawa wajen aiki ba su da rauni a tsoffin ofisoshin su, wannan ne ya sanya aka tura su zuwa muhimman ma’aikatun biyu.

A Larabar nan ne Buhari ya kori ministan Noma da raya karkara Muhammad Sabo Nanono da ministan lantarki Sale Mamman.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!