Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Covid-19: KAROTA ta gargadi masu shirin taron daurin aure

Published

on

Hukumar lura da ababan hawa ta jihar Kano KAROTA ta gargadi wasu iyali dake shirin gudanar da bikin daurin aure a wannan mako.
Cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun Sadik Farouk Yola a madadin shugaban hukumar Baffa Babba Danagundi ta ce ta samu wasu iyalai da suka hadar da Alhaji Hassan Badeh, da Alhaji Ibrahim Muhammad da kuma Alhaji Abdullahi Kwamaret Bako, kan su dakatar da shirin su na gudanar da shagalin bikin aure da suke shirin yi.
A cewar KAROTA ta samu labarin cewa za a gayyato baki daga birnin tarayya Abuja da kuma Legas a don hakan take tunasar da su cewa akwai dokar hana cakuduwar jama’a a Kano.


Wakilin mu Nasiru Salisu Zango ya tuntubi Alhaji Ibrahim Badeh daya daga cikin wadanda ke shirin wannan daurin aure, inda ya shaida masa cewa daman basu gayyaci kowa daga wajen Kano ba, daurin auren kadai za a yi a watse, ba tare da cinkoso ba.

Karin labarai:

KAROTA ta kama babbar mota makare da giya

Direbobi sun maka KAROTA da ‘Yan sanda a gaban kotu

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!