Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Kasar Amurka ta bukaci Najeriya da ta sauya dabarun yaki da kungiyar boko haram

Published

on

Kasar Amurka ta bukaci Najeriya da ta sauya dabarun da ta ke amfani da su a yanzu haka wajen yakar yan kungiyar Boko Haram la’akari da yadda mayakan ke kokarin bijirewa dabarun da ake amfani da su.

 

Guda daga cikin manyan hafsan sojin kasar Amurka da ke halartar taron hafsoshin kasan kasashen Afrika wanda kuma shi ke jagorantar taron da ke ci gaba da gudana a Abuja Laftanal kanal Sean McClure ya ce kamata ya yi a samar da sabbin dabaru matukar ana bukatar gaggauta fattattakar mayakan na Boko Haram.

 

Amurka dai na neman yin uwa da makarbiya ne waje ganin ta taimakawa kasashen Afrika da gabas ta tsakiya wajen kammala yakar ayyukan ta’addanci.

 

Kanal McClure ya ce ayyukan ta’addanci a kassahen Afrika da suka kunshi na Boko Haram a Najeriya da Nijar, Kamaru da kuma Chadi da kuma na Al-Qaeda a Mali ka iya zama tarihi matukar aka hada hannu wuri guda.

 

A baya-bayan nan dai Amurkan na nuna damuwa matuka kan ayyukan ta’addancin da ke faruwa a Nahiyar Afrika, inda ta kaddamar da wani atisayen soji a Jamhuriyar Nijar daga kasashe 26 da suka kunshi 12 na Afrika da kuma 14 daga sauran sassan duniya da nufin yakar ayyukan ta’addanci a yankin Sahel.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!