Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Ƙetare

Kotun Amurka ta saki tsohon shugaba Donald Trump

Published

on

Kotu a birnin New York ta saki tsohon shugaban Amurka Donald Trump ba tare gindaya wasu sharudda ba a shari’ar da aka fara a kansa dangane da zarge-zarge masu alaka da biyan makuden kudade gabanin zaben shekarar 2016.

Trump wanda ya musanta dukkanin tuhume -tuhumen 34 da ake yi masa yayin zaman shri’ar da ake yi masa karkashin jagorancin mai shari’a Juan Merchant wanda ke matsyin karon farko a tarihin Amurka da wani shugaba tsoho ko mai ci ya taba gurfana gaban kotu inda ya bayyana shari’ar da makarkashiya gareshi kuma abun kunya ga Amurka .

Inda alkalin ya dage shari’ar zuwa watan Junairun 2024 ko da yake lauyoyin Trump sun bukaci dawo da shari’ar kurkusa,lura da yadda lokacin shari’ar yayi daidai da lokacin zaben fidda gwamani da tunkara zaben shugaban kasa na shekarar,zaben da Trump ke shirin sake tsayawa takara .

Cilkin tuhum- tuhume 34 da ake akan Trump dai harda biyan makudan kudade mabanbanta mutane wandanda ake gani suka kai su shuga nasara a zabe na 2016 ciki harda jarumar fina finan batsa da yayi mu’amala da ita da kuma wani dake da bayani yadda tsohon shugaban ke da wani da da ya haifa ba tare da aure ba.

Sabon Tuhume tuhume Trump ya musanta akwai tayar da hankali tare da tunzura magoya bayan sa bayan faduwa zabe 2019 wanda ya kai ga rikicin capital da yayi sanadiyar mutuwar mutane shida.

 

 

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!