Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Wasanni

Kasar Mali ta lashe kofin Afurka ta matasa yan kasa da shekaru 20

Published

on

Kasar Mali ta lashe kofin Afurka ta matasa ‘yan kasa da shekara 20 bayan da ta samu galaba Akan kasar Senegal da ci uku da biyu a bugun daga kai sai mai tsaron raga.

Tun farko dai kasashen biyu sun tashi a wasa da ci daya da daya, wannan kuma wani ramuwar gayya ce da kasar ta Mali ta yi bayan tun farko Senengal din ta doketa da ci biyu da nema a wasan rukuni.

A wani ci gaban kuma, hukumar kwallon kafa ta Afrika CAF ta amince da amfani da VAR a gasar cin kofin nahiyar Afrika da za a yi Bana a kasar Masar a watan Yuni zuwa watan Yuli.

Hukumar ta amince da amfani da na’urar ne jiya a jamhuriyar Niger bayan kammala gasar cin kofin Afrika na matasa ‘yan kasa da shekara 20, kuma wannan shine karo na farko a tarihin gasar cin kofin nahiyar Afrika da za a yi amfani da na’urar,

A wasan damben gargajiyar da ake yi a gidan wasa na Ado Bayero Square wasannin da aka kara a jiya,

Dan Sadauki da Arewa ya buge Autan Mai Takwasara Guramada.

Shagon Sojoji daga Arewa da Bahagon Kudu sun yi turmi biyu baba kisa.

Bahagon mai Takwasara ya buge Bahagon Onwando daga Arewa.

Shagon dan Bature daga Arewa ya kashe bahagon mai takwasara daga Guramada.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!