Connect with us

Labarai

Katsina: Yan sanda sun kama mutanen da ake zargi da yi wa yan bindiga safarar makamai

Published

on

Rundunar yan sandan Jihar Katsina ta kama wasu da ake zargi da yi wa ’yan ta’adda safarar makamai, inda aka kwato babbar bindiga da harsasai sama da guda dubu daya.

 

Wannan na cikin wata sanarwa da Kwamishinan Tsaro da Harkokin cikin gida na jihar Katsina, Dakta Nasir Mu’azu, ya fitar a Litinin din makon nan.

 

Sanarwar ta bayyana cewa, jami’an ƴan sanda daga garin Ingawa ne suka tare wata mota kirar Golf da ake yin amfani da ita wajen jigilar makaman a kan hanyar Ingawa zuwa karkarku, inda aka cafke mutane biyu da ake zargi, Abdulsalam Muhammad mai shekaru 25 da Aminu Mamman mai kimanin shekaru 23, dukkansu mazauna Ƙaramar Hukumar Safana.

 

Sanarwar ta kara da cewa, makaman da aka kwato sun hada da babbar bindiga da harsasai 1,063 na bindiga kirar AK-47. 

 

Gwamnatin Jihar Katsina ta yaba da ƙoƙarin ’yan sanda, tare da tabbatar da cewa za ta ci gaba da tallafa musu wajen yakar ta’addanci da sauran manyan laifuka.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!