Connect with us

Labarai

Kebbi: Lakurawa sun hana manoma sayar da dabbobi don siyan injinan Noma

Published

on

Rahotonni daga jihar Kebbi, sun tabbatar da cewar ‘yan ta’addar Lakurawa sun shiga garuruwa fiye da 10 a ƙaramar hukumar Augie ta jihar inda suka gargaɗi jama’a da ka da su ƙara sayar da shanunsu domin sayan injinan huɗa da ke amfani da Man fetur.

Ta cikin wasu bayanan sirri da wani mazaunin yankin ya fitar, ya shaida cewa suna sayar da shanun ne domin su sayi motar noman shinkafa amma a yanzu basu da iko sai dai su hakura domin su tsira da rayukan su, sakamakon barazana da suke fuskanta daga ‘Yan ta’addar. 

Shaidun gani da ido a yankin na Augie sun ce Lakurawan  kan  shiga gari a kan Babura, dauke da bindigu kuma sukan kwashe dabbobi a cewar ‘yan garin da suka nemi a sakaye sunansu.

Yanzu haka dai ana  ci gaba da zaman dar-dar a  yankin, yayin da jama’a ke roƙon gwamnati da hukumomin tsaro su tashi tsaye domin kawo ƙarshen wannan matsala da ta dabaibaye rayuwar su da amfanin gonakin su.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!