Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Kotu: ta bada belin tsohon gwamnan jihar Ekiti kan kudi naira miliyan 50

Published

on

Babbar Kotun tarayya ta Jihar Lagos karkashin mai Shari’a Mujisola Olatoregun ta ba da belin tsohon gwamnan Jihar Ekiti Ayodele Fayose kan kudi Naira Miliyan 50 a yau.

Haka zalika mai Shari’a Mujisola Olatoregun ta sanya sharadin mutanen biyun da za su tsaya ma sa dole su bayar da shaidar biyan harajin shekaru 3, baya ga wadancan kudade Naira miliyan 50.

Sannan ta bukaci Ayodele Fayose ya mikawa kotun Fasfonsa na tafiye-tafiye.

Tun da fari Lauyan Fayose Kanu Agabi ya nemi Kotun ta ba da belin tsohon gwamnan na Ekiti, kasancewar bisa radin kasa ya mika wuya ga hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta EFCC baya ga kasancewarsa mutum mai mutunci.

Sai dai EFCCn ta nuna rashin amincewarta da ba da belin bayan da ta ce Fayose ya samu rakiyar wasu fusatattun ‘yan bangar siyasa zuwa ofishinta, da ke da muradin farwa hukumar.

Kuma har yanzu hukumar na ci gaba da zakulo irin kadarorin da ya mallaka ta hanyar halasta kudaden haram.

Tsohon gwamnan na Ekiti na fuskantar tuhume-tuhume guda 11 da suka danganci halasta kudaden haram da suka kai Naira biliyan daya da miliyan 200, baya ga karbar kudi Naira biliyan daya da miliyan 200 ta haramtacciyar hanya don gudanar da yakin menan zabensa a shekar 2014.

 

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!