Labarai
Kotu ta bayar da belin Nasir El-Rufa’i

Tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai ya samu beli daga babbar kotun tarayya da ke Abuja kan kudi Naira miliyan 100.
Mai shari’a Joyce Abdulmalik ce ta bayar da belin a ranar Litinin, inda ta ce dole ne wanda zai tsaya masa ya kasance mazaunin yankin Maitama ko Asokoro a Abuja, sannan ya ajiye takardar mallakar gida ta asali a kotu.
Kotun ta kuma umarci wanda zai tsaya masa ya kasance ma’aikacin gwamnatin tarayya mai matakin aiki daga Grade Level 17 zuwa sama, tare da gabatar da shaidar albashi na akalla watanni uku da kuma takardar tabbatarwa daga manajan bankinsa.
You must be logged in to post a comment Login