Connect with us

Labarai

Ku yafe mana bashin da kuke bin mu – Buhari ga kasashen turai

Published

on

Shugaban ƙasa Muhammadu Buhari ya buƙaci ƙasashen turai da cibiyoyin kudi na duniya da su yafewa ƙasashen afurka basukan da suke binsu.

 

A cewar sa, hakan zai taimaka gaya wajen daƙile halin da ƙasashen nahiyar suka shiga sanadiyar cutar corona.

 

Muhammadu Buhari ya bayyana hakan ne lokacin da ya ke jawabi a wajen taro kan harkokin kudi a ƙasashen nahiyar afurka a birnin Paris da ke ƙasar Faransa.

 

A cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun babban mataimaki na musamman ga shugaban ƙasa kan harkokin yada labarai Malam Garba Shehu ta ruwaito shugaba Buhari na cewa kasashen afurka na cikin tsaka mai wuya sanadiyar cutar covid-19.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!