Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

KannyWood

Kun san jaruman da sukafi yawan mabiya a Kannywood?

Published

on

Dandalin sada zumunta na Instagram shi ne shafin da jarumai da kuma masu hurda da masana’antar shirya fina-finan Hausa ta Kannywood sukafi maida hankali akan sa.

Babu shakka ga duk wanda ke neman wata gulma ko tsokaci game da masana’antar Kannywood to kawai yayi amfani da shafin Instagram domin ganin dukkan wainar da ake toyawa a masana’antar.

A yayinda shekara ta 2019 ke bankwana Freedom Radio ta bibiyi manyan jaruman dake amfani da dandalin na Instagram inda muka zakulo muku mutane goma sha daya da suke da yawan mabiya a masana’antar.

Jaruma Rahma Saudau

Rahma Sadau: Ita ce wadda tafi kowane jarumi a masana’antar Kannywood yawan mabiya a dandalin Instagram inda take da mabiya har kimanin miliyan daya da dubu dari bakwai, ba iya nan Rahma Sadau ta tsaya ba, domin kuwa ita ce ta kere dukkan al’ummar Hausawa yawan mabiya a dandalin na Instagram.

Rahma Sadau tana cikin jaruman da akafi cece kuce akansu a kafafan sada zumunta a wannan shekara da muke bankwana da ita ta 2019.

Labarai masu alaka:

Hotunan fitsara: Rahma Sadau ta ce ita ba ‘yar Kano ba ce- Kannywood

Jaruma Hadiza Gabon

Hadiza Gabon: ita ce ta biyu wajen yawan mabiya a shafin Instagram inda take da yawan mabiya har kimanin miliyan daya da dubu dari biyar.

Rikicin Hadiza Gabon da jaruma Amina Amal shi ne ya kara yayata Hadiza Gabon a shekarar 2019.

Jaruma Nafisa Abdullahi

Nafisa Abdullahi: tana da yawan mabiya har miliyan daya da dubu dari uku.

Jarumi Ali Nuhu

Ali Nuhu: Wanda ake yiwa lakabi da sarkin Kannywood yana da mabiya har miliyan daya da dubu dari uku.

Labarai masu alaka:

Ni da Ali Nuhu laifunmu ne ke haifar da matsala a Kannywood –Adam Zango

Jarumi Adam A. Zango

Adam A. Zango: shi ke marawa Ali Nuhu baya wanda yake da mabiya miliyan daya da dubu dari biyu a dandalin na Instagram, a wannan shekarar da muke bankwana da ita dai an ta faman tafka dambarwa tsakanin Ali Nuhu da Adam Zango wadda har ta kaisu gaban kotu, kafin daga bisani dattawan Kannywood su samar da maslaha a tsakaninsu.

A yanzu haka dai tuni Adam Zango ya ce ya fice daga masana’antar shirya fina-finan Hausa ta Kannywood sannan yayi hijira daga jihar Kano, inda ya koma jihar Legas da zama.

Kazalika a kwanakin baya anyi ta cece kuce kan batun daliban da Adam A. Zango yace ya dauki nauyin karatunsu a wata makaranta dake Zariya.

Labarai masu alaka:

Da gaske Adam Zango ya dauki nauyin karatun dalibai?

Jaruma Fati Washa

Fati Washa: Itama tana da mabiya har miliyan daya da dubu dari biyu a dandalin Instagram, a kwanakin baya ne dai akayi ta cece kuce a kafafan sada zumunta kan wasu hotuna da ta wallafa a shafinta na Instagram.

Kazalika a shekarar da muke bankwana da ita ne aka karrama Fati Washa da lambar yabo ta gwarzuwar Kannywood a wani taron baje kolin fina-finai da akayi a Birtaniya.

Sai dai shi ma cece kuce ya biyo baya sakamakon wani hotonsu da jaruma Rahma Sadau ta wallafa a shafin Twitter.

Jaruma Maryam Booth

Maryam Booth: Itama tana da mabiyar har miliyan daya da dubu dari biyu a dandalin Instagram.

Jaruma Hafsat Idris

Hafsat Idris: Wadda akafi sani da Barauniya tana da mabiya har miliyan daya da dubu dari biyu.

A farkon watan Disambar da muke ciki ne aka yita cece kuce kan wani hoto da jaruma Hafsat Idris ta wallafa da mahaifinta bayan da Allah yayi masa rasuwa, inda jama’a suka rika cewa ta dauki hoton bayan da ya rasu zargin da ta musanta inda ta ce sun dauki hoton ne tun yana da ransa.

Labari masu alaka:

Ban dauki “selfie” da gawar mahaifina ba -Hafsat Idris

Jarumi Sadiq Sani Sadiq

Sadiq Sani Sadiq: Jarumin da yayi fice wajen fitowa a kowane irin mataki a shirin Film yana da mabiya har miliyan guda.

Jaruma Maryam Yahya

Maryam Yahya: Matashiyar Jarumar da tauraruwarta tafi haskawa a shekarar 2019 tana da mabiya har miliyan guda.

Jama’a na kallon cewa shigowar Maryam Yahya masana’antar ya haifar da karin shigowar kananan yara domin a dama dasu a harkar fina-finan Hausa.

Kazalika ita ma Maryam Yahaya ta haifar da cece kuce akanta a kafafan sada zumunta tun daga batun haduwarta da dan kwallon kafar nan Pogba a kasar Saudia, da kuma wani bidiyonta da aka dauka ba tare da ta sani ba, aka kuma rika yadawa a kafafan sada zumunta.

Labarai masu alaka:

Kun san abinda ya hana jaruma Maryam Yahya aure?

Na taba yin soyayya da Maryam Yahaya a baya –Mai Shadda

Jaruma Aysha Humair

Aysha Humaira: Tayi fice a dandalin sada zumunta na Instagram kafin daga bisani a fara ganinta a fina-finan Hausa, yanzu haka tana da mabiya har miliyan guda a dandalin na Instagram.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!