Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Kungiyar JOHESU ta fara aikin yajin aikin sai baba-ta-gani

Published

on

Gamayyar Kungiyar ma’aikatar lafiya ta JOHESU, ta ce a daren jiya Talata ta fara yajin aikin sai baba-ta-gani a fadin kasar nan.

Shugaban kungiyar Josiah Biobelemoye ne ya bayyana hakan yayin zantawa da manema labarai a birnin tarayya Abuja a jiya.

Biobelemoye ya kuma ce, tuni kungiyar ta umarci mambobinta da ke aiki a dukkannin Asibitocin kasar nan su tsunduma yajin aikin tare da kaucewa duk wani abu da ka iya kawowa kungiyar cikas a kan yajin aikin da ta fara.

Ya kuma kara da cewa ba za su janye yajin aikin ba har sai gwamnatin tarraya ta biya musu bukatunsu da su cimma yarjejeniya a kai, a ranar biyar ga watan Fabrairun da ya gabata.

Shugaban kungiyar Josiah Biobelemoye ya ce daga cikin bukatun na su akwai inganta albashin ma’aikata da samar da kayayyakin aiki Asibitocin gwamnatin.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!