Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Nan da kwanaki 15 idan gwamnati bata biya mana bukatun mu ba zamu fara yajin aiki-JOHESU

Published

on

Gamayyar kungiyoyin ma’aiktan lafiya na Najeriya JOHESU sun bawa gwamnati wa’adin kwanaki 15, kan ta biya musu bukatun su ko su tsunduma yajin aikin sai Baba ta gani.

Shugaban kungiyar Kwamared Biobelemoye Josiah, ne ya fadi hakan a cikin wata wasika da ya aike wa Ministan Kwadago Sanata Chris Ngige, da sauran masu ruwa da tsaki yau Asabar a Abuja.

Josiah ya ce, matukar wa’adin kwanaki 15 ya cika gwamnati ba ta biya musu bukatun su ba, ya zama dole su tafi yajin aiki duba da halin da membobinsu ke ciki.

Wannan na zuwa ne bayan yajin aikin da Likitoci masu neman kwarewa ke yi da kuma wa’adin kwanaki 21 da Kungiyar Likitoci ta kasa ta ba gwamnatin tarayya don fara yajin aikin gama gari a duk fadin kasar.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!