Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Yanzu-yanzu: NLC ta janye yajin aikin da ta shirya tsunduma yau a Kano

Published

on

Ƙungiyar ƙwadago ta ƙasa reshen jihar Kano NLC ta janye yajin aikin data ƙudiri farawa daga ƙarfe goma sha biyu na daren yau.

Mataimakin shugaban ƙungiyar na kasa Kwamred Najeeb Yasin ne ya bayyana hakan yayin da gamayyar ƙungiyoyin ƙwadagon ke ganawa da manema labarai a daren Laraba.

Najeeb Yasin ya ce, janye yajin aikin ya biyo bayan tattaunawar da ƙungiyoyin su ka yi da Gwamnan Kano Dakta Abdullahi Umar Ganduje.

A cewar sa, Gwamna Abdullahi Ganduje ya amince da dawo da kuɗin ma’aikatan da aka yanke albashin su a watannin baya.

Ya ƙara da cewa, a watan da muke ciki na Afrilu ko watan Mayu mai kamawa Gwamnatin zata dawo da kuɗaɗen da ta yanke.

A cewar sa, Gwamnatin Kano ta ce bata buƙatar sake dawo da biyan mafi ƙarancin albashi na naira dubu goma sha takwas ga ma’aikatanta.

Saboda haka ƙungiyoyin suka yanke shawarar janye yajin aikin da suka ƙudiri farawa daga karfe goma sha biyu na daren Laraba bakwai ga watan Afrilu.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!