Connect with us

Labarai

Kungiyar ma’aikatan lafiya ta JOHESU a Najeriya ta tsunduma yajin aiki

Published

on

Hadaddiyar Kungiyar Ma’aikatan Lafiya JOHESU da Kungiyar Kwararru a Fannin Kiwon Lafiya  a Najeriya sun fara yajin aiki a yau Asabar.

 

Kungiyoyin sun ce gazawar gwamnatin kasar wajen aiwatar da sabon tsarin albashin ma’aikatan lafiya da kuma kawo karshen matsalolin da suka jima suna korafi  a kan su ne musabbabin tafiya yajin aikin.

 

Bayanin hakan na kunshe ne a wata sanarwa da shugaban JOHESU na Kasa, Kwamared Kabiru Ado Minjibir, ya sanayawa hannu.

 

Yajin aikin na kungiyoyin na zuwa ne a daidai lokacin Kungiyar Likitoci Masu Neman Kwarewa ta kasa ta ke nata yajin aikin saboda rashin biyan wasu bukatunta.

 

Ana fargabar yajin aikin da kungiyoyin ke yi zai durkusar da harkar kiwon kafiya a asibitocin gwamnatin tarayya da na jihohi da dama a fadin Najeriya.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!