Connect with us

Labarai

Kungiyar manoman shinkafa RIFAN ta dakatar da shirin ba da rance a Kano

Published

on

Kungiyar manoman shinkafa ta kasa RIFAN ta dakatar da shirin ba da rance ga manoma na Ancho borrowers a nan Kano nan take ba tare da bata lokaci ba.

Shugaban kungiyar reshen jihar Kano Alhaji Abubakar Haruna Aliyu ne ya sanar da hakan yayin zantawa da manema labarai.

Ya ce, dakatar da shirin na ancho borrowers zai taimaka wajen gudanar da cikakken bincike kan zargin da hukumar karbar korafe-korafe da yaki da cin hanci da rashawa ta jihar Kano ke yi kan shugabannin kungiyar ta RIFAN.

Alhaji Abubakar Haruna Aliyu ya kuma ce kungiyar tana alhinin sanar da dukkan nin mambobinta cewa daga yanzu, an dakatar da gudanar da shirin na ancho borrowers a nan Kano zuwa wani lokaci.

Ya kara da cewa uwar kungiyar ta kasa ce ta ba da umarnin dakatar da shirin anan Kano don bai wa hukumomi dama da su gudanar da bincike game da zargin almundahana.

Shirin ancho borrowers dai shiri ne na gwamnatin tarayya da aka kirkiro da nufin bai wa manoma bashi ta hannun babban bankin kasa CBN.

 

 

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!