Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Majalisar dokoki ta gayyaci Akpabio kan badakalar NDDC

Published

on

Majalisar wakilai ta gayyaci ministan kula da yankin NIGER Delta Sanata Godswill Akpabio da ya gurfana gaban kwamitinta mai kula da yankin na Niger Delta don karin haske kan ayyukan hukumar ta NDDC.

Majalisar ta dau wannan mataki ne biyo bayan zarge-zarge da tsohuwar shugabar hukumar NIGER Delta Dr Joi Nunieh ta yi kan Mr Akpabio bayan da ta gurfana gaban kwamitin a yau.

A jiya Alhamis ne dai ‘yan sanda su ka yi yunkurin kama tsohuwar shugabar hukumar ta NDDC a gidanta da ke garin Fatakwal, kafin daga bisani gwamnan jihar Rivers Nyeson Wike ya ceto ta.

Wata majiya ta shaidawa manema labarai cewa watakila yunkurin kama da tsohuwar shugabar hukumar kula da yankin na Niger Delta yana alaka ne da yunkurin hanata halartar zaman da kwamitin kula da yankin na Niger Delta na Majalisar wakilai ke yi don gano gaskiyar zargin almundahana a hukumar

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!