Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Kungiyar manyan malaman jami’o’i ta kasa ASUU sun daidata da gwamnatin tarayya

Published

on

Kungiyar manyan malaman jami’o’I ta kasa ASUU ta dai-daita da gwamnantin tarayya a jiya litinin don ganin an kawo karshen yajin aikin da aka kwashe tsahon lokaci ana gudanarwa.

Sanata Chris Ngige wanda shine Ministan kwadago, ne ya bayyana hakan jim kadan bayan kammala taron tattaunawar da aka gudanar tsakanin su da kungiyar ta ASUU.

Ngige ya kuma ce an samu abin da ake bukata na kyakyawar matsaya a yayin gudanar da taron, inda ya ce gwamnantin tarayya ta ware naira biliyan 15 da miliyan 4 don biyan kudaden albashi wanda yana cikin manyan bukatun malaman.

Sannan ya ce gwamnati zata ci gaba da duba manyan bukatun su da kuma duba yiwuwar biya musu cikin dan kankanin lokaci.

Da ya ke jawabi shugaban kungiyar na kasa Farfesa Biodun Ogunyemi ya ce kwamitin gudanarwar kungiyar zai sake zama don yin duba kan bukatun nasu wanda zai yi dai-dai da matsayar da aka cimma da gwamnantin tarayya.

Sannan ya ce za’a janye yajin aikin ne idan kwamitin gudanarwar kungiyar ya kammala zaman sa, sai dai bai fadi lokacin da kwamitin zai zauna ba.

Malaman jami’a dai sun tsunduma yajin aiki ne tun ranar 4 ga watan Nuwambar shekarar bara kan abinda suka kira rashin cika musu alkawurran da gwamnantin tarayya ta daukar musu a yajejeniyar da su sha kullawa.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!