Connect with us

Labarai

Kwankwaso ya zargi gwamnatin tarayya da gaza magance matsalar tsaro

Published

on

Tsohon Gwamnan Kano kuma dan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar NNPP, a zaben shekarar 2023 , Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya soki gwamnatin tarayya, da cewa ta gaza wajen magance matsalar tsaro da ke ƙara yaduwa a faɗin Najeriya.

Ta cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na Facebook, Sanata Kwankwaso ya ce, yadda gwamnati ta bar jihohi su kafa ƙungiyoyin sa-kai ba tare da horo na musamman ba, ya kara tabarbara tsaron kasar da ya jawo yawaitar kananan makamai a hannun batagari da rura wutar rikice-rikice.

Haka kuma, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, ya bayyana takaicin sa kan wariya da rarrabuwar kai da ƙabilanci da tsangwama da cin zarafi da ke faruwa a wasu yankunan Najeriya tare da yawaitar kalaman ƙiyayya a kafafen sada zumunta.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!