Labarai
Kwastam ta kama magungunan jabu masu ɗauke da lambar NAFDAC

Hukumar yaki da fasa kyauri ta Najeriya Kwastam, ta kama magungunan jabu masu ɗauke da lambar rajistar NAFDAC ta bogin, miyagun ƙwayoyi da kuma magungunan da wa’adinsu ya ƙare, waɗanda jimillar ƙimarsu bayan biyan haraji ta kai Naira biliyan 53.39 a tashar jiragen ruwa ta Apapa da Legas.
Hukumar ta bayyana kamen a matsayin wani babban ci gaba a ƙoƙarinta na kare lafiyar al’umma da kuma tsaron ƙasa.
Da yake jawabi yayin miƙa waɗannan miyagun ƙwayoyi da magungunan da wa’adinsu ya ƙare ga hukumomin da abin ya shafa a hedikwatar rundunar Apapa a ranar Laraba, Shugaban Hukumar Kwastam ta Ƙasa, Bashir Adewale Adeniyi, ya ce an samu nasarar kama kayayyakin ne sakamakon tattara bayanan sirri da kuma haɗin gwiwa tsakanin Kwastam da NDLEA.
A cewarsa, kayayyakin da aka kama sun haɗa da sama da Tan 6.7 na tabar wiwi da aka ɓoye a cikin kwantena biyu masu ƙafa 40 tare da motocin da aka shigo da su da kuma kayan gyaran motoci.
Sauran abubuwan da aka kama sun haɗa da kwalabe 339,800 na maganin tari mai ɗauke da sinadarin Codeine, kwantenoni da dama na magungunan da wa’adinsu ya ƙare, maganin yara na Powder, da kuma magungunan jabu masu ɗauke da lambobin rajistar NAFDAC na bogi.
You must be logged in to post a comment Login