Labarai
Shugaban Tinubu zai ƙaddamar da littafin tunawa da marigayi Muhammadu Buhari

Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, zai ƙaddamar da wani littafin tunawa da marigayi tsohon shugaban ƙasa, Muhammadu Buhari, a yayin bikin cikar shekara guda da rasuwarsa.
Shugaban Kwamitin Shirye-shiryen Taron kuma tsohon Sakataren Gwamnatin Tarayya, Boss Mustapha, ya ce za a gudanar da addu’o’in ne a tsakanin mabiya addinin Musulmi da Kirista.
Boss Mustapha ya bayyana cewa littafin mai taken Tributes and Condolences in Honour of Muhammadu Buhari ya ƙunshi saƙonnin ta’aziyya daga shugabannin ƙasashe, jami’an diflomasiyya da fitattun jagororin siyasa daga sassa daban-daban na duniya.
Ya ce Shugaba Tinubu ne zai ƙaddamar da littafin, wanda daga bisani za’a dauki nauyin raba shi kyauta ga al’ummar kasa.
You must be logged in to post a comment Login