Labarai
Shugaba Tinubu ya kaddamar da sauye-sauye a shirin NYSC

Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, ya kaddamar da wasu sabbin sauye-sauye ga shirin hidimar kasa NYSC, da nufin sabunta tsarin domin ya fi mayar da hankali kan bunkasa tattalin arziki da koyon sana’o’i da kuma inganta al’adun Najeriya.
Sabbin sauye-sauyen sun hada da rage mayar da hankali kan atisayen soja da aka saba yi a sansanonin hukumar ta NYSC, tare da kara horas da matasa kan sana’o’i da fasahar zamani da kasuwanci domin su samu damar dogaro da kansu bayan kammala shirin na hidimar kasa.
Haka kuma, gwamnatin ta ce, za a inganta sansanonin NYSC, tare da karfafa yin amfani da kayan gargajiya na cikin gida, a matsayin wata hanya ta bunkasa masaku da kuma kare al’adun Najeriya.
You must be logged in to post a comment Login