Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Kano

Likitoci sun gano abinda ke janyo ciwon hauka

Published

on

Wani bincike da likitocin kwakwalwa suka gudanar ya gano cewa, cutar damuwa watau Depression shi ne kan gaba wajen sanya mutane na kamuwa da ciwon Hauka.

Wata ma’aikaciya a asibitin kula ma masu lalurar kwakwalwa na Dawanau da ke nan Kano Hajiya Amina Idris Muhammad ce ta bayyana hakan ta cikin shirin ‘’Barka da Hantsi’’ nan Freedom Radio.

Ta ce cutar ta damuwa na jefa mutane cikin larurori da dama inda take kama mutane sakamakon sanya yawan damuwa a ransu bisa wani abu da ya sha musu kai.

Haka kuma ta kara da cewa, matasan wannan yanki na Arewacin Najeriya na fama da yawan tunane-tunanen al’amuran yau da kullum wanda hakan ke sanya su fadawa cikin wannan matsala.

Da yake nasa jawabin, Malam Nura Husain wanda shi ma ya kasance a cikin shirin, ya bayyana cewa a matsayinsu na masu kula da masu lalurar kwakwalwar, suna fama da matsalar rashin baiwa marasalafiyar magungunansu yadda ya kamata har ma da rashin mayar da su asibitin akan lokaci.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!