Connect with us

Labarai

Lokaci ya yi da matasan Afrika za su fara yin jagoranci- Obasanjo

Published

on

Tsohon Shugaban Najeriya Olusegun Obasanjo, ya jaddada buƙatar  cewar lokaci ya yi da matasan Afrika zasu fara riƙe muƙaman jagoranci a faɗin nahiyar.

Ya bayyana hakan ne a yayin taron wayar da kan mtasaka kan shugabanci mai taken Presidential Youth Mentorship Retreat da aka gudanar a Abeokuta, babban birnin  Jihar Ogun, ƙarƙashin cibiyar ci gaban Matasa a Ɗakin Tarihi na Shugaba Olusegun Obasanjo OOPL.

Tsohon shugaban ya jaddada cewa lokaci ya yi da matasa za su tashi tsaye su jagoranci nahiyar Afrika domin makomarsu ta dogara da abin da suka yi a yau.

Ya yin taron, tsohon Babban Hafsan Tsaron kasar nan , Janar Martin Luther Agwai mai ritaya, ya ce barazanar da Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yi kan zargin kisan Kiristoci a Nijeriya, ya zama gargaɗi ga shugabanni su ƙara ƙaimi wajen yaƙi da rashin tsaro.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!