Connect with us

Labarai

Ma’aikatar Muhalli ta Tarayya ta yi gargaɗi kan samun ambaliya

Published

on

Ma’aikatar Muhalli ta Tarayya ta sake yin sabon gargaɗi kan yiwuwar samun ambaliya Ruwa a wasu jihohi.

A wata takarda da Daraktan Sashen kula da Kwazazzabai da Ambaliya da yankunan gaɓar Ruwa, Alhaji  Usman Abdullahi Bokani, ya sanya wa hannu,  aka rabawa manema labarai an bayyana cewa ana sa ran ruwan sama mai yawa tsakanin 1 zuwa 3 ga watan Oktoba, 2025, wanda ka iya haddasa ambaliya.

Jihohin da ambaliyar ka iya shafa sun haɗa da Adamawa, Kebbi, Bauchi, Zamfara, Sakkwato, Kaduna da Neja, inda a jihar ta Kebbi ake tsammanin samun ambaliyar garuruwan Argungu, Bagudu, Gwandu, Jega, Kalgo, Kamba, Kangiwa da Birnin Kebbi.

Sai jihar Kaduna dake da yankin  Jaji da Zariya kawai, yayin da a Jihar Neja ake tsammanin samun hakan a  Magama da Sarkin-Pawa, sai garuwan  Mubi, Gusau da Azare dake jihohin Adamawa da Bauchi da Zamfara.

Ma’aikatar , ta shawarci jama’a da ke zaune kusa da koguna ko rafuka su ɗauki matakan kariya ko su bar waɗannan wurare domin guje wa ambaliyar.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!