Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Mace-macen aure su ne manyan kalubalen da muke fuskanta – Hisbah

Published

on

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta ce mace-mace aure da sauran matsalolin auren na daga cikin manyan kalubalan da suke fuskanta a cikin aikinsu.

Mukaddashiyar Kwamnandan hukumar mai kula da bangaren mata Malama UmmuKulsum Kassim ce ta bayyana hakan jim kadan bayan kammala shirin Barka da Hantsi na nan Freedom Radio, wanda ya yi duba kan matsalolin zamantakewar aure wanda aka yi a jiya Juma’a.

Malama Ummukulsum ta kara da cewa rashin daukar ragamar kula da iyalai daga bangaren mazaje na daga cikin abubuwan da ke haddasa wannan matsala.

Ta kara da cewa wajibi ne mazaje su rinka taimakawa mata wajen tarbiyyantar ‘ya’yansu domin bunkasa rayuwarsu.

Malama UmmuKulsum Kassim ta shawarci iyaye su dage sosai wajen baiwa ‘ya’yansu ilimin addinin musulunci yadda ya dace domin kyautata rayuwarsu a nan duniya da kuma gobe kiyama.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!