Labarai
Ganduje zai dauki matakin ladaftarwa akan shugabannin tashar mota
![](https://freedomradionig.com/wp-content/uploads/2020/03/ganduje-latest.jpg)
Gwamnatin Jihar Kano ta baiwa shugabannin tashar mota ta Rijiyar Zaki wa’adin mako guda da su tabbatar da tsaftace ciki da wajenta, ko kuma ta dauki matakin ladaftarwa a kansu.
Kwamishinan muhalli na Jihar Kano Dakta Kabiru Ibrahim Getso ne ya ba da umarnin yayin duban tsaftar muhalli na kasuwanni da asibitoci da ma’aikatun gwamnati, wanda ake gudanarwa a karshen ko wane wata.
Kwamishinan wanda babban sakatare a ma’aikatar Adamu Abdu Faragai ya wakilta, ya ce gwamnati ba za ta lamunci barin datti a wuraren hada-hadar jama’a ba, a don haka za ta dauki mataki kan masu karya dokar tsaftar muhalli.
You must be logged in to post a comment Login