Labaran Wasanni
Magoya bayan Manchester United na fatan a sallami mai horar da kungiyar kafin wasan Tottenharm
![](https://freedomradionig.com/wp-content/uploads/2021/10/images-46.jpeg)
Wasu magoya bayan kungiyar kwallon kafa na Manchester United sun ce suna fatan hukumar gudanarwar kungiyar za ta Kori mai horar da ita Ole Gunnar Solskjær sakamakon rashin a bin a zo a gani a ƙungiyar ke yi.
A baya bayannan dai Manchester United ta yi rashin nasara a hannun Liverpool da ci 5-0 a filin wasanta na Oldtrafrod.
A cewar su kafin wasanni 2 masu zafi da kungiyar za ta kara nan gaba da Tottenham da kuma kungiyar Manchester city ya kamata a sallameshi.
A na ganin cewa mai horos da Manchester United bazai iya tsallake wasannin da zai fafata ba da kungiyoyin guda biyun ba.
You must be logged in to post a comment Login