Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Majalisar dinkin duniya ta nemi matasa su kasance masu neman na kai

Published

on

Majalisar dinkin duniya ta bukaci matasa da su kasance masu neman na kansu hadi da jajircewa wajen neman ilimi da nufin inganta tattalin arzikin kasashen su.

Wannan na cikin wata sanarwa da majalisar ta sanyawa hannun a wani bangare na bikin ranar matasa ta duniya, da ake gudanarwa a yau Talata.

A cewar majalisar, matasa su ne kashin bayan kowacce al’umma baya ga lalubobo hanyoyin inganta rayuwarsu a nan gaba.

Akan kan ne wakilin mu Awwal Hassan Fagge ya jiyo ra’ayoyin wasu matasa a nan kwaryar birnin Kano, dangane da irin kalubalan da suke fuskanta.

Wani masanin nazarin hallayar dan Adam da ke Jami’ar Bayero a nan Kano, DR Abdullahi Mai Kano Madaki, ya bayyana hanyoyin da matasa za su bi don inganta rayuwarsa.

DR Mai-Kano Madaki ya kuma bukaci gwamnotoci a dukkannin matakai, da su kara kaimi wajen ciyar da matasa gaba a fannoni daban-daban  na rayuwa.

Taken bikin na bana shi ne, hadin kan matasa don inganta rayuwarsu ta gaba.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!