Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Majalisar ɗinkin duniya za ta magance ƙarancin abinci a Arewacin Najeriya

Published

on

Majalisar ɗinkin duniya ta kafa kwamitin kar-ta-kwana da zai yi haɗin gwiwa da wasu ƙungiyoyin agaji don magance matsalar ƙarancin abinci a Arewacin Najeriya.

Babban Sakataren majalisar António Guterres, ne ya bayyana hakan ta cikin wata sanarwa da mai Magana da yawun sa Stéphane Dujarric ta fitar.

António Guterres ya ce ƙungiyoyin da majalisar za su mayar da hankali ne, wajen ganin sun ƙara inganta harkokin noma a Najeriya ta yadda za’a magance fargabar da ake tunani na samun karancin abinci.

Sanarwar ta ce ƙungiyoyin za su yi aiki kafaɗa da kafaɗa da gwamnatin tarayya da kuma na jihohi domin ganin an samu nasara kan shirin da za a gudanar.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!