Connect with us

Labarai

Majalisar Dokokin Kano ta amince da dokoki 2 da suka shafi inganta fannin lafiya

Published

on

Majalisar Dokokin Jihar Kano ta amince da dokoki guda biyu da suka shafi inganta harkokin lafiya a jihar, bayan da suka tsallake karatu na biyu.

Dokar farko ta shafi tabbatar da ƙwarewa da horar da ungozoma na gargajiya domin ba su takardar shaidar aiki ta doka. Wanda hakan zai taimaka wajen rage mace-macen mata masu juna biyu da jarirai a yankunan karkara.

Haka kuma, majalisar ta karanta dokar kafa hukumar kula da dakunan gwaje-gwajen lafiya, wacce za ta tabbatar da ingantaccen binciken cututtuka da daidaita ayyukan dakunan gwaje-gwaje a fadin jihar.

Bayan karatu na biyu, kakakin majalisar, Alhaji Jibril Isma’il Falgore, ya tura dokokin zuwa kwamitocin da suka dace domin ƙarin nazari kafin amincewa da su gaba ɗaya.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!