Connect with us

Labarai

NDLEA ta cafke wasu ababen fashewa a hanyar zuwa Zamfara

Published

on

Hukumar yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi NDLEA ta ce, ta kama wasu abubuwan fashewa a kan hanyar zuwa jihar Zamfara da aka yi niyyar shigar da su.

Hukumar ta bayyana hakan ne a wata sanarwa da ta fitar a karshen mako.

Ta ce, jami’an ta da ke aikin sintiri a kan hanyar Kaduna zuwa Zariya ne suka kama wata mota wadda ke dauke da abubuwan fashewan bayan da ta tashi daga jihar Nasarawa zuwa Zamfara.

NDLEA ta ce, binciken da suka yi game da motar ne ya kai suka gano abubuwan fashewar har guda 942 a daure a cikin buhu tare da kama wani da ake zargi mai suna Nura Sani dan kimanin shekaru 30.

Haka kuma Shugaban hukumar Janar Buba Marwa mai ritaya, ya bayar da umarnin tsare  mutumin da ake zargi da kuma abubuwan da aka gano a wurinsa, don ci gaba da bincike.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!