Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Jigawa

Majalisar Jigawa ta bada aikin kwangilar matatun ruwa

Published

on

Majalisar zartaswa ta jihar Jigawa ta bada kwangilar gina sababbin matatun ruwa guda shida akan kudi naira miliyan 173.

Kwamishinan yada labarai na jihar, Bala Ibrahim ne ya bayyana yayin zantawa da manema labarai a bayan kamala taron majalisar zartarwa ta jihar a yau alhamis a birnin Dutse.

Bala Ibrahim ya ce, majalisar ta amince da bada aikin domin kara inganta ruwan sha a wasu garuruwan da ke fama da karancin ruwan sha a jihar.

Kwamishinan ya kara da cewa garuruwan da zasu amfana da aikin ruwan sun hada Basirka, Sabon-Garin-‘yaya’, da Bosuwa, Dakaiyawa, Gidan Lage, da Dangyatun, Maimazari da kuma Sabongarin Birnin Kudu.

Ya kara da cewa majalisar zartarwa ta kuma amince da gina sabbain matatun ruwa a garin Kila, Jigawar-Marka, Kunkuru, Garkon-Alli da kuma Dan Faramtama.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!