Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Majalisar Kano ta amince Ganduje ya ciyo bashin Naira Biliyan Goma Sha Biyar

Published

on

Majalisar dokokin jihar Kano ta amince kananan hukumomin jihar arba’in da hudu da su ciyo bashin Naira Biliyan Goma Sha Biyar domin da shirin ba da ilimi kyauta da gwamnatin jihar ta kaddamar a shekarar da ta gabata.

Hakan ya biyo bayan amincewa da rahoton kwamitin kula da kananan hukumomi wanda dan majalisa mai wakiltar karamar hukumar Kiru, Kabiru Hassan Dashi, ya gabatar a yau.

Da ya ke zantawa da manema labarai bayan kammala zaman majalisar, Kabiru Hassan Dashi, wanda Kuma shine mataimakin shugaban masu rinjaye na majalisar, ya ce, kudaden za su taimakawa kananan hukumomin wajen aiwatar da shirin ba da ilimi kyauta da gwamnatin Kano ta aiwatar a bara.

“Yanzu kananan hukumomin za su iya gina sababbin ajujuwa da sayan kayayyakin sawa na dalibai saboda samun kudaden”Inji Kabiru Hassan Dashi.

A shekaran jiya litinin ne gwamnan Kano Dr Abdullahi Umar Ganduje ya turo da wasikar da ya bukaci majalisar ta amince don kananan hukumomi su ciyo bashin naira miliyan dari uku da arba’in Kowannensu, don aiwatar da shirin ba da ilimi kyauta.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!