Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Kano

Kananan hukumomin jihar Kano za su ciyo bashin Naira Biliyan Goma Sha Biyar

Published

on

Gwamnan Kano Dr. Abdullahi Umar Ganduje ya aikawa majalisar dokokin jihar Kano da wata wasika da ke neman ciyo bashi ga kananan hukumomin jihar Kano arba’in da hudu.

Da ya ke karanta wasikar,   shugaban majalisar dokokin jihar Kano, Abdul’aziz Garba Gafasa, ya ce, kananan hukumomin za su ciyo bashin ne don samar da kudade da za su yi amfani da su wajen shirin ba da ilimi kyauta da gwamnatin Kano ta kaddamar a shekarar da ta gabata.

“Kowace karamar hukuma za ta ciyo bashin naira biliyan dari uku da arba’in, a daya daga cikin bankunan kasuwanci na kasar nan.

Lauyoyi sun nemi majalisar Kano ta jingine batun dokar kafa masarautu 4

Majalisar Kano zata aiwatar da dokar cin zarafin bil adama

Kotu ta dakatar da gwamnatin Kano daga aiwatar da sabuwar majalisar sarakuna

Bayan karanta wasikar, shugaban majalisar Abdulaziz Garba Gafasa, ya tambayi mambobin majalisar, ko sun amince da a karbi wasikar da gwamna ya aiko da shi, wanda ba tare da bata lokaci ba, su ka amince da hakan.

Wakilin mu na majalisar dokokin jihar Kano, Abdullahi Isah, ya ruwaito cewa, daga nan ne Kuma majalisar ta umarci kwamitin ta da ke kula da kananan hukumomi da ya je ya nazarci wasikar da ke kunshe da bayanan yadda za a ciyo bashin da  kudin ruwa da yadda za a rika biyan bashin.

 

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!